Gambo was born in Fagada Babba, Mayyama Local
Government, Kebbi State, Nigeria. His real date of birth is still under the
cloud, but he claimed to be Seventy years old (70) as at 2002/2003. He died in
the year 2016. By his oral testimony, he might be between 85/86 years old by
the year 2018/2019 respectively. His pen name is Alhaji Muhammadu Gambo Mai Waqar Varayi. He was an accidental singer as he
did not learn the art of singing from any singer of his contemporaries.
Monday, October 14, 2019
Wane Ne Narambaxa? Ibrahim Narambaxa Buhari Maidangwale Abdulkadir Tubali (1890-1963)
Abu-Ubaida Sani
October 14, 2019
0
‘Narambaɗa’ laƙabi ne
da ake yi masa ga karyar farautarsa da ya yi wa suna Rambaɗa. An haife shi a garin Tubali
shekarar 1890. Sunansa na yanka Ibrahimu, sunan mahaifinsa Buhari Maidangwale,
sunan kakansa Abdulƙadir, sunan
mahaifiyarsa Riba.[1]
Sunan kakarsa mace Binta. Mahaifinsa Babarbare ne daga ƙasar
Nijar, mahaifiyarsa mutunniyar Badarawa ce gidan Sarkin Makaɗa Ɗangwamna.
Don haka, Narambaɗa
Kakkaɓan Gara Ga: “Laccar Makirce-Makircen Shi’a Ta Farfesa Umar Labɗo
Abu-Ubaida Sani
October 14, 2019
0
Asalin
Shi’a daga Yahudu ne, makamashin wutarta na asali ƙabilanci.
A tarihance, mutanen Farisa sun ɗauki Larabawa
bayi, don haka a ƙasarsu
aka fara yaga wasiƙar
Annabi (SAW). Babban takobin yaɗa Shi’a shi ne siyasa, a shiga
rigarta a yi tashintashina da ta’addanci. Abubuwan da su Abdullahi bn Saba’
suka haddasa tsakanin Ali (RTA) da A’isha (RTA) da Mu’awiyya (RTA) da musibar
Karbala abin kula ne.
Wurin Da Babu Ƙasa Nan Ake Gardamar Kokuwa (Sharhin Littafin: Da ‘Yan Nijeriya da Buhun Gero Wa Ya Fi Yawa?)
Abu-Ubaida Sani
October 14, 2019
0
Hausawa
na cewa: “Komi ya ɓace maza ka biɗo
shi”. Babban tunaninsu a kan haka shi ne, wuyar aiki ba a fara ba. A kowane
lokaci mutane ke jayayya ana buƙatar raba gardama. Idan sa-in-sa ya
yawaita, gaskiya ce ba ta bayyana ba. Da ta leƙo, ita ce raba
gardama. Labarin masu yunƙurin fayyace da buhun gero da ‘yan
Nijeriya wa ya fi yawa, ya bice duniyar kafafen yaɗa
labarai na BBC da ƁOA da RFI da jaridun ƙasa da kafafen
yaɗa
labarai na jihohi. Da masoyansu, da masu mamakinsu, da masu musunsu, da masu
adawa, dole su yarda da cewa, wannan al’amari ya gawurta kuma ya yi tasiri ga
duniyar lokacinmu. Ganin irin ƙwazon matasan da suka assasa wannan
batu, suka ba lokacinsu, da tunaninsu, na ganin sai sun kuranye yanar da ke
ciki, ya san a yi wa wannan takarda taken: Wurin da babu ƙasa nan ake
gardamar kokuwa”. Yanzu sai a biyo mu a ji ina salka ka tsatsa.
Ruwa Na Ƙasa Sai Ga Wanda Bai Tona Ba (Hisabin Waƙar Malam Babba na Ƙofar Gabas Azare)
Abu-Ubaida Sani
October 14, 2019
0
Tun fil azal
karambanin leƙo abin da ya faku Bahaushe na kiransa
duba. A wata fassara idan ta shafi amfanin da wuri ana ce masa “arwa”. Bayyanar
Musulunci da wasu malamai suka durmuya ciki, a zauna, a harɗe, a share ƙasa, a
goge, ya sa ake yi masa suna da “Bugun ƙasa”. A
waƙar da muke nazari Alhaji Shata ya yi
amfani da “duba”. Ta kowace fuska aka yi karambanin gano gobe, ta carbi ce, ko ta
taurari, ko ta bugun ƙasa, ko
ta hisabi ko ta duban motsin wasu tsuntsaye da dabbobi, sunansa “duba”.
Kunya Ginshiƙin Tsaron Ƙasa Da Bunƙasarta
Abu-Ubaida Sani
October 14, 2019
0
Kunyar
da ke tsakanin yara da manya ita ta wanzar da zaman siyasar
shugabancin ƙasar
Hausa ta fi kowace biyayya tsakanin masu mulki da moro. Da Musulunci ya zo, kunyar ta faɗaɗa
tsakanin malamai da ɗalibai.
Tsare wannan kunyar ya hana wanzuwar yi wa masu iko tawaye da zanga-zanga, ya
toshe rigingimu irin na addini tsakanin mabiya da shugaba ko malamai. Rashin
kunya ne yin sa-in-sa da shugaba ko malami.
Muhimmancin Haɗin Kai Ga Duban Watan Ramalana
Abu-Ubaida Sani
October 14, 2019
0
Umurnin
da Manzo (SAW) ya ba Bilal na ya yi sanarwa ga ganin watan da aka shaida masa
wata hujja ce ta tabbatar da hukuma ke da ikon sanarwa na ganin wata. Waɗanda suka zo wa Sayyidina
Umar bakinsu buɗe ranar da yake azumi da jama’arsa a matsayinsa
na Sarkin Musulmi, ya tambaye su, suka ce wata suka gani, wata hujja ce da ta
kore jiran sanarwa ga Muminai idan sun yi ido huɗu
da wata. Matsalar da ke rarraba muna kai a nan ita ce, samun sanarwa na ganin
watan wani wuri ko wata ƙasa
daga fitattun gidajen rediyon BBC da VOA da RFI France da DW Germany
da CNN da makamantansu.
Tags
# HAUSA
Continue Reading