Monday, October 14, 2019

Folklore And Economic Security In Nigeria: (Alhaji Gambo Fagada a Radical Whistle Blower in Financial Crimes and Economic Genocide Matters)

October 14, 2019 0


Gambo was born in Fagada Babba, Mayyama Local Government, Kebbi State, Nigeria. His real date of birth is still under the cloud, but he claimed to be Seventy years old (70) as at 2002/2003. He died in the year 2016. By his oral testimony, he might be between 85/86 years old by the year 2018/2019 respectively. His pen name is Alhaji Muhammadu Gambo Mai Waqar Varayi. He was an accidental singer as he did not learn the art of singing from any singer of his contemporaries.

Wane Ne Narambaxa? Ibrahim Narambaxa Buhari Maidangwale Abdulkadir Tubali (1890-1963)

October 14, 2019 0


‘Narambaɗa’ laƙabi ne da ake yi masa ga karyar farautarsa da ya yi wa suna Rambaɗa. An haife shi a garin Tubali shekarar 1890. Sunansa na yanka Ibrahimu, sunan mahaifinsa Buhari Maidangwale, sunan kakansa Abdulƙadir, sunan mahaifiyarsa Riba.[1] Sunan kakarsa mace Binta. Mahaifinsa Babarbare ne daga ƙasar Nijar, mahaifiyarsa mutunniyar Badarawa ce gidan Sarkin Makaɗa Ɗangwamna. Don haka, Narambaɗa

Kakkaɓan Gara Ga: “Laccar Makirce-Makircen Shi’a Ta Farfesa Umar Labɗo

October 14, 2019 0


Asalin Shi’a daga Yahudu ne, makamashin wutarta na asali ƙabilanci. A tarihance, mutanen Farisa sun ɗauki Larabawa bayi, don haka a ƙasarsu aka fara yaga wasiƙar Annabi (SAW). Babban takobin yaɗa Shi’a shi ne siyasa, a shiga rigarta a yi tashintashina da ta’addanci. Abubuwan da su Abdullahi bn Saba’ suka haddasa tsakanin Ali (RTA) da A’isha (RTA) da Mu’awiyya (RTA) da musibar Karbala abin kula ne.

Wurin Da Babu Ƙasa Nan Ake Gardamar Kokuwa (Sharhin Littafin: Da ‘Yan Nijeriya da Buhun Gero Wa Ya Fi Yawa?)

October 14, 2019 0


Hausawa na cewa: “Komi ya ɓace maza ka biɗo shi”. Babban tunaninsu a kan haka shi ne, wuyar aiki ba a fara ba. A kowane lokaci mutane ke jayayya ana buƙatar raba gardama. Idan sa-in-sa ya yawaita, gaskiya ce ba ta bayyana ba. Da ta leƙo, ita ce raba gardama. Labarin masu yunƙurin fayyace da buhun gero da ‘yan Nijeriya wa ya fi yawa, ya bice duniyar kafafen yaɗa labarai na BBC da ƁOA da RFI da jaridun ƙasa da kafafen yaɗa labarai na jihohi. Da masoyansu, da masu mamakinsu, da masu musunsu, da masu adawa, dole su yarda da cewa, wannan al’amari ya gawurta kuma ya yi tasiri ga duniyar lokacinmu. Ganin irin ƙwazon matasan da suka assasa wannan batu, suka ba lokacinsu, da tunaninsu, na ganin sai sun kuranye yanar da ke ciki, ya san a yi wa wannan takarda taken: Wurin da babu ƙasa nan ake gardamar kokuwa”. Yanzu sai a biyo mu a ji ina salka ka tsatsa.

Ruwa Na Ƙasa Sai Ga Wanda Bai Tona Ba (Hisabin Waƙar Malam Babba na Ƙofar Gabas Azare)

October 14, 2019 0



Tun fil azal karambanin leƙo abin da ya faku Bahaushe na kiransa duba. A wata fassara idan ta shafi amfanin da wuri ana ce masa “arwa”. Bayyanar Musulunci da wasu malamai suka durmuya ciki, a zauna, a harɗe, a share ƙasa, a goge, ya sa ake yi masa suna da “Bugun ƙasa”. A waƙar da muke nazari Alhaji Shata ya yi amfani da “duba”. Ta kowace fuska aka yi karambanin gano gobe, ta carbi ce, ko ta taurari, ko ta bugun ƙasa, ko ta hisabi ko ta duban motsin wasu tsuntsaye da dabbobi, sunansa “duba”.

Kunya Ginshiƙin Tsaron Ƙasa Da Bunƙasarta

October 14, 2019 0


Kunyar da ke tsakanin yara da manya ita ta wanzar da zaman siyasar shugabancin ƙasar Hausa ta fi kowace biyayya tsakanin masu mulki da moro. Da Musulunci ya zo, kunyar ta faɗaɗa tsakanin malamai da ɗalibai. Tsare wannan kunyar ya hana wanzuwar yi wa masu iko tawaye da zanga-zanga, ya toshe rigingimu irin na addini tsakanin mabiya da shugaba ko malamai. Rashin kunya ne yin sa-in-sa da shugaba ko malami.

Muhimmancin Haɗin Kai Ga Duban Watan Ramalana

October 14, 2019 0



Umurnin da Manzo (SAW) ya ba Bilal na ya yi sanarwa ga ganin watan da aka shaida masa wata hujja ce ta tabbatar da hukuma ke da ikon sanarwa na ganin wata.  Waɗanda suka zo wa Sayyidina Umar bakinsu buɗe ranar da yake azumi da jama’arsa a matsayinsa na Sarkin Musulmi, ya tambaye su, suka ce wata suka gani, wata hujja ce da ta kore jiran sanarwa ga Muminai idan sun yi ido huɗu da wata. Matsalar da ke rarraba muna kai a nan ita ce, samun sanarwa na ganin watan wani wuri ko wata ƙasa daga fitattun gidajen rediyon BBC da VOA da RFI France da DW Germany da CNN da makamantansu.