Showing posts with label HAUSA. Show all posts
Showing posts with label HAUSA. Show all posts

Tuesday, August 16, 2022

Ba A Wane Bakin Banza: Gurbin Daular Gobir Da Gobirawa A Farfajiyar Sudaniyya

August 16, 2022 0

Gobir tsohuwar Daula ce da ta shiga gwagwarmaya da daulolin duniyar Sudaniyya. Burin wannan bincike ƙyallaro wasu daga cikin dalilan da suka ɗaga Daular Gobir da Gobirawa sama ga sauran dauloli. An yi garkuwa da fitattun ayyuka wallafaffu da waɗanda ba a wallafa ba tare da taimakon yawon rangadi da tattaunawa da dafa kafaɗar adabin baka da rubutacce. Binciken ya gano cewa, Daular Gobir cin gashin kanta take yi kuma Bahaushiyar Daula ce. Bugu da ƙari, ta ƙi ta aminta da tarihihin Bayajidda ya ratsa Daularta. Dabarun yaƙin Daular Gobir da siyasar sarautunta sun yi tasiri sosai ga daulolin Sudaniyya. Babu Daula daga cikin daulolin Sudaniyya da ta yi yaƙe-yaƙen Daular Gobir. Ƙasar Gobir, Gobirawa suka sari abarsu kuma su suka fara sarauta a ciki duk wani baƙo da ya zo ciki sai dai auratayya ta narkar da shi ya zama Bagobiri. Binciken ya gano, rushewar Alkalawa bai rusa masarautun Gobirawa ba da haɗin kansu. Akwai buƙatar samun cikakken kundin tarihin Gobirwa da al’adunsu domin a taskace shi a kundin tarihin duniya. Gobir ta cancanci haka idan aka yi la’akari da tarihinta da ƙarfin ikonta.

Wednesday, September 29, 2021

Ɗiyan Sarauta A Tafashen Makaɗa Alhaji Musa Ɗanƙwairo

September 29, 2021 0

Alhaji Musa Ɗanƙwairo Maradun na daga cikin fitattun makaɗan fada da suka makaro a ƙasar Hausa. Binciken wannan takarda ya ɗora shi a cikin rukunin makaɗan sarauta bisa taliyon salsalar waƙoƙin gidansu da ya gada, ya ɗora a kai. Binciken takarda ya tsaya a kan jigon “zambo”, ko a cikin jigon ya taƙaita ga “zambon ɗiyan sarauta”. An saurari waƙoƙin Ɗanƙwairo da yawa na sarauta, an karanta wasu da aka taskace, an yi amfani da mataimaka wajen bincike da tattaunawa domin a tattaro hujjojin da za a tattauna. Hujjojin da aka tattaro sun tabbatar da ɗiyan sarauta su ne aji na farko ga zambo a waƙoƙin sarauta na Ɗanƙwairo. Binciken ya gano, duk wata waƙa ta sarauta tana da turaku uku! Yabo, zambo da tarihi. Su uku duka, zambo ya fi su amo da ratsa zukata. Duk wata waƙar sarauta da ba a ratsa zambo ga ɗiyan sarauta ba, ba ta waƙu ba, a sake bitar ta. Zambon da ake yi wa ɗiyan sarauta kashi uku ne: Da-kai-nike, saye, da bisa-kan-mai-tsotsayi. Takardarmu ta gano ga dukkanin rukunan zambo, ba a saka iyaye, ko gidan sarauta, ko ‘yan uwan wanda ake yi wa zambo, a ciki. A ɗan yunƙurin kafa hujjoji an kasa takardar cikin fasali goma sha huɗu (14) haɗi da gabatarwa da naɗewa. An yi amfanid a ɗiyan waƙa goma sha shida (16) don daidaita bayani.

Tuesday, September 22, 2020

Zamfarawa a Diwanin Narambaɗa

September 22, 2020 0

 Takardar da aka gabatar a taron ƙasa da ƙasa mai taken: Zamfara Kingdom: Social and Political Transformation from 14th Centuary to Date. Organized by Faculty of Arts and Islamic Studies Usmanu Danfodiyo University, Sokoto, 25th – 28th February, 2020, at Usmanu Danfodiyo University Auditorium, Sokoto

Monday, October 14, 2019

Hausa Da Hausawa A Duniyar Кarni Na Ashirin Da Ɗaya (Amsa Kiran Majalisar Ɗinkin Duniya (UN) Ga Ranar Hausa Ta Duniya – Litinin 26 Ogusta, 2019)

October 14, 2019 0


Mutanen da ke magana da “Hausa” a matsayin harshen gado uwa da uba, kaka da kakanni su ne ‘Hausawa’. Samun tussan asalinsu na tun fil azal a garuruwan da Hausawa suka kafa, wata hujja ce ta zama Bahaushe. “Bahaushe” tilo ne na mai magana da Hausa a matsayin harshen gado, “Hausawa” jam’i ne na “Bahaushe”. A binciken magabatanmu, ‘Bahaushe’ shi ne:

Gaskiya A Кi Ki, A So Ki

October 14, 2019 0


Farfesa Aliyu Muhammad Bunza ya rubuta wannan waƙa ranar 8 ga watan Ogusta, shekara ta 2019. Tana da adadin baituka arba’in da biyu (42). Ta kasance ‘yar ƙwar huɗu.

Tsaro A Nijeriyar Кarninmu: Lokacin Abu A Yi Shi

October 14, 2019 0



Tunanin Bahaushe a kan tsaro ya shafi tsaron lafiyar jiki da rayuwar da ke ɗawainiya da ita; tsaron ƙasa da tattalin arzikinta; wadatuwar abinci da ayyukan yi ga masu tsaro da ƙasar da ake ɗawainiyar tsarewa. Ke nan, tunanin Bahaushe na faɗar ‘tsaron kaya ya fi ban cigiya’, ya tabbatar da kasancewar tsaro makamin farko a rayuwar ɗan Adam. A fashin baƙin tsaro za mu ce, shi ne, samun walwala da sakewa da more wa ƙasa ga ɗan ƙasa, da samun cikakkiyar natsuwa da za ta gargaɗi kowace irin barazana da fargaba da tashin-tashina ga ‘yan ƙasa da baƙin da suka baƙunce ta. Samun wannan cikakken aminci shi ne tsaro ga ƙasa.

Wane Ne Narambaxa? Ibrahim Narambaxa Buhari Maidangwale Abdulkadir Tubali (1890-1963)

October 14, 2019 0


‘Narambaɗa’ laƙabi ne da ake yi masa ga karyar farautarsa da ya yi wa suna Rambaɗa. An haife shi a garin Tubali shekarar 1890. Sunansa na yanka Ibrahimu, sunan mahaifinsa Buhari Maidangwale, sunan kakansa Abdulƙadir, sunan mahaifiyarsa Riba.[1] Sunan kakarsa mace Binta. Mahaifinsa Babarbare ne daga ƙasar Nijar, mahaifiyarsa mutunniyar Badarawa ce gidan Sarkin Makaɗa Ɗangwamna. Don haka, Narambaɗa

Kakkaɓan Gara Ga: “Laccar Makirce-Makircen Shi’a Ta Farfesa Umar Labɗo

October 14, 2019 0


Asalin Shi’a daga Yahudu ne, makamashin wutarta na asali ƙabilanci. A tarihance, mutanen Farisa sun ɗauki Larabawa bayi, don haka a ƙasarsu aka fara yaga wasiƙar Annabi (SAW). Babban takobin yaɗa Shi’a shi ne siyasa, a shiga rigarta a yi tashintashina da ta’addanci. Abubuwan da su Abdullahi bn Saba’ suka haddasa tsakanin Ali (RTA) da A’isha (RTA) da Mu’awiyya (RTA) da musibar Karbala abin kula ne.

Wurin Da Babu Ƙasa Nan Ake Gardamar Kokuwa (Sharhin Littafin: Da ‘Yan Nijeriya da Buhun Gero Wa Ya Fi Yawa?)

October 14, 2019 0


Hausawa na cewa: “Komi ya ɓace maza ka biɗo shi”. Babban tunaninsu a kan haka shi ne, wuyar aiki ba a fara ba. A kowane lokaci mutane ke jayayya ana buƙatar raba gardama. Idan sa-in-sa ya yawaita, gaskiya ce ba ta bayyana ba. Da ta leƙo, ita ce raba gardama. Labarin masu yunƙurin fayyace da buhun gero da ‘yan Nijeriya wa ya fi yawa, ya bice duniyar kafafen yaɗa labarai na BBC da ƁOA da RFI da jaridun ƙasa da kafafen yaɗa labarai na jihohi. Da masoyansu, da masu mamakinsu, da masu musunsu, da masu adawa, dole su yarda da cewa, wannan al’amari ya gawurta kuma ya yi tasiri ga duniyar lokacinmu. Ganin irin ƙwazon matasan da suka assasa wannan batu, suka ba lokacinsu, da tunaninsu, na ganin sai sun kuranye yanar da ke ciki, ya san a yi wa wannan takarda taken: Wurin da babu ƙasa nan ake gardamar kokuwa”. Yanzu sai a biyo mu a ji ina salka ka tsatsa.

Ruwa Na Ƙasa Sai Ga Wanda Bai Tona Ba (Hisabin Waƙar Malam Babba na Ƙofar Gabas Azare)

October 14, 2019 0



Tun fil azal karambanin leƙo abin da ya faku Bahaushe na kiransa duba. A wata fassara idan ta shafi amfanin da wuri ana ce masa “arwa”. Bayyanar Musulunci da wasu malamai suka durmuya ciki, a zauna, a harɗe, a share ƙasa, a goge, ya sa ake yi masa suna da “Bugun ƙasa”. A waƙar da muke nazari Alhaji Shata ya yi amfani da “duba”. Ta kowace fuska aka yi karambanin gano gobe, ta carbi ce, ko ta taurari, ko ta bugun ƙasa, ko ta hisabi ko ta duban motsin wasu tsuntsaye da dabbobi, sunansa “duba”.

Kunya Ginshiƙin Tsaron Ƙasa Da Bunƙasarta

October 14, 2019 0


Kunyar da ke tsakanin yara da manya ita ta wanzar da zaman siyasar shugabancin ƙasar Hausa ta fi kowace biyayya tsakanin masu mulki da moro. Da Musulunci ya zo, kunyar ta faɗaɗa tsakanin malamai da ɗalibai. Tsare wannan kunyar ya hana wanzuwar yi wa masu iko tawaye da zanga-zanga, ya toshe rigingimu irin na addini tsakanin mabiya da shugaba ko malamai. Rashin kunya ne yin sa-in-sa da shugaba ko malami.

Muhimmancin Haɗin Kai Ga Duban Watan Ramalana

October 14, 2019 0



Umurnin da Manzo (SAW) ya ba Bilal na ya yi sanarwa ga ganin watan da aka shaida masa wata hujja ce ta tabbatar da hukuma ke da ikon sanarwa na ganin wata.  Waɗanda suka zo wa Sayyidina Umar bakinsu buɗe ranar da yake azumi da jama’arsa a matsayinsa na Sarkin Musulmi, ya tambaye su, suka ce wata suka gani, wata hujja ce da ta kore jiran sanarwa ga Muminai idan sun yi ido huɗu da wata. Matsalar da ke rarraba muna kai a nan ita ce, samun sanarwa na ganin watan wani wuri ko wata ƙasa daga fitattun gidajen rediyon BBC da VOA da RFI France da DW Germany da CNN da makamantansu.

Gurbin Harshen Fashin Baƙi Ga Mai Tafsiri

October 14, 2019 1


Addinin Musulunci ya yi fiye da shekaru aru-aru da leƙo Afirka idan aka yi la’akari da ɓullar addinin a Makka da tarihin Hijira ta farko da ta biyu[1]. A hasashen tarihi, daulolin ƙasar Hausa maƙil suke da mutane a zamanin da Musulunci ya bayyana a duniya.  Tarihin yadda ya shigo ƙasar Hausa abin kirdado ne tsakanin Daular Borno da Daular Mali da Daulolin Larabawan Sahara da kuma ɗaiɗaikun ‘yan kasuwa…

Thursday, January 10, 2019

Don Me Ake Karatun Hausa?

January 10, 2019 0



Bisa ga al’adar ɗaliban harshen, ya kamata in ce: don me ake karatun harshe? Sanin cewa, masana sun yi wa harshe tarkakken nazarin da ɗalibi zai ratsa ya samu waraka ga bayanin harshe ko ilimin harsuna, sai na zaɓi in yi bara da Hausa.[1] Haka kuma, ba ina nufin Hausa ba harshen ba ne,[2] buƙatata ita ce, ƙyallaro dalilan da zai sa, mai harshe, ya nazarci harshensa, ko ya nazarci wani harshe a matsayin fagen karatu da neman shahara a ciki. A ganina, gajeren tunanin ‘yan bayan fage ga duniyar ilmi a koyaushe yana nuna musu, wace fa’ida ke cikin karatun harshenka na gado da ka tashi ciki, ka balaga ciki, kuma kana rayuwa a ciki?[3] Masu irin wannan fahintar…

Kuka A Faifan Nazari: Laluben Diddigin Bahaushen Kuka Da Ƙunshiyar Lafazinsa

January 10, 2019 0

A iya sanina, wannan ɗan bincike sabo ne, saboda rashin samun wani da ya gabace shi a fagen nazarin Hausa. Duk da haka, abin da aka gina bincike a kansa “kuka” ya girmi duk wani mai bincike da zai yi bincike a kansa. Tunanin kowane mai tunani, ba zai fice da’irar al’adarsa da adabinsa da aka gina cikin harshen da yake rayuwa da shi. Sanin haka ya sa na gayyato ƙwararrun mawaƙan Hausa (20) [14 na baka, 6 marubuta], na sarrafa ɗiyan waƙoƙinsu (34). Cikin wannan fafitikar, na yi garkuwa da karin magana (3), kirari (1), ƙagaggen labari (1), waƙoƙin dandali (3) domin daidaita akalar bincike. Bisa hasken waɗannan kayan aiki (62) aka ci nasarar gano…

Wednesday, January 9, 2019

Bitar Karatun Hausa A Ƙarni Na Ashirin Da Ɗaya (Ƙrn. 21): (Wurin Da Babu Ƙasa Ake Gardamar Kokuwa)

January 09, 2019 0


The paper is a historical review of Hausa studies in Nigerian academia. In the struggle, relevant related literatures were critically examined to justify the dare need of an updated progress report. In this study, an advanced Hausa study is the desired target to conjugate Hausa on the rating scale of Nigerian academic standard. Similarly, tertiary institutions, Universities and research centers handling Hausa academic Activities are the umbilical cord of the paper. To be more precise, the paper concentrates on the Nigerian factor in the subject under review. Gladly, it peeps through nineteen Nigerian Universities, thirty eight other tertiary institutions and four research centers to update the progress report of the journey so far. The review captures forty indigenous Nigerian Professors of Hausa studies, and forty…

Wednesday, January 2, 2019

Wane Ne 'Dan Ta’adda?sava

January 02, 2019 0

 Gajeren tunanin da ke ga ɗan Adam shi ya sa Larabawa ke ce masa Insan wadda aka cirato daga kalmar Nisyan, mai nufin mantuwa. Mutum zai kafa dokar wani abu, da baya ya zo ya saɓa mata. Wannan dalili ne ya sa Hausawa ke cewa, mai dokar barci ya koma angaje. Matsalolin tsaro sai daɗa taɓarɓarewa suke yi, a koyaushe gara jiya da yau, shekaran jiya ta fi jiya, yau ta fi gobe. Babban abin nufi a nan shi ne , ƙoƙarin dangantawa wata al’umma da ke wata nahiya mai riƙe da wani addini alhakin ringingimun da ke wakana a duniyar zamaninsu. Yau, babu, ɓata gari sai Musulmi. Babu ɗan ta’adda sai Musulmi. Bab...

Bugun Gaba (Salon A San Ni, A Ji Ni, A Gane Ni Ne Wane)

January 02, 2019 0


Maƙasudin wannan xan bincike shi ne, yi wa wasu salailan adabi sunan da ya dace da su domin ƙara faxaxa bincike da nazari. Nazarin ya yi ƙoƙarin tabbatar da samuwar “Salon Bugun Gaba” cikin kowane sashe na adabin Bahaushe. An tsara aikin cikin manyan sassa tara (9), ƙananan sassa goma sha xaya (11). An ziyarci makaxan baka (8), marubuta waƙoƙi huxu (4), marubuci xaya (1) domin a tabbatar da samuwar Salon Bugun Gaba. An sarrafa karin magana (3), xiyan waƙar baka goma sha uku (13), rubutattun waƙoƙi huxu (4) domin a daddagi bagiren sosai a xebe kokanto...

Gurbin Sarkin Musulmi A Ganin Watan Azumi

January 02, 2019 1


Godiya ta tabbata ga Allah Mahaliccin halittun da ba su ƙidayuwa ga wani bawa daga cikin bayinSa. Ya ƙago sammai ya ƙawata (ta duniyarmu) da hasken taurari domin amfaninmu. Ya ba mu rana da wata domin daidaita ibadojinmu gwargwadon savawarsu a duniyarmu. Burina a wannan ‘yar takarda shi ne, lalubo wasu matsalolin ganin watan Ramalana da irin gurbin da shari’armu ta yi wa Sarkin Musulmi na kowace ƙasa ta Musulmi a ciki. Wannan xan yunƙuri an yi shi da nufin cike wani givi daga cikin kusurwowin da Shaixan ke kutsowa ya yaudare mu ta fuskar haxin kanmu. Matsalolin da ke tattare da ganin wata a duniya…